Ambasada Hajiya Samira Bala Usman Ta Zama Tauraruwar Hausa

Daga Ibrahim Muhammad

Sakamakon kyakkyawar shaida ta irin ɗimbin gudunmuwa da take bayarwa, Gidauniyar Hausa da haɗin gwiwar Hausawan Duniya Charity, ta tabbatar da Ambasada Hajiya Samira Bala Usman a matsayin Tauraruwar Hausa da cigaban Hausawan Duniya a wani taro da aka gudanar na Gidauniyar a Kano.

Da take zantawa da ‘yan jarida bayan karɓar shaidar, Hajiya Samira Bala Usman, ta bayyana farin cikinta da murna bisa shaida da aka ba ta ta zama ɗaya daga cikin ‘yan Gidauniyar Hausa da Hausawan Duniya Charity duba da yadda ƙungiya ce da take da himmar samar wa Hausawan Duniya haɗin kai da cigaba.

Ta ƙara da cewa ta gamsu mutuƙa da irin tsare-tsaren da Gidauniyar take yi masu ma’ana wajen gina cigaban al’umma.

Ta ce tana ƙoƙari wajen hana barace-barace da tallafa wa marayu da kuma haɗa kan al’ummar Hausawa a duk inda suka samu kansu a duniya, kowa ya san ɗan’uwansa sanan suna kuma bunƙasa al’adu da harshen Hausa.

Ambasada Hajiya Samira Bala Usman Tauraruwar ta Hausa da Hausawan Duniya ta yi nuni da cewa dama Gidauniyar ta Hausa da haɗin kan Hausawa na duniya tana da jajicewa wajen cigaban al’ummar Hausawa, kuma su ma da suke a cikinta za su ba da gudunmawa sosai domin kan Hausawa ya haɗu a ko’ina suke a kowace ƙasa a fadin duniya.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun