Gwamnan Kano Jinjina Wa Kwamishinan Da Ya Ajiye Aikinsa

Daga Ibrahim Muhammad

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da ajiye aiki da Injiniya Muhammad Diggol, ya yi a matsayinsa na Kwamishinan ma’aikatar bibiyar aiyuka nan take.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya raba wa manema labarai.

Tun a farkon mulkinsa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Muhammad Diggol a matsayin Kwamishinan sufuri, kafin daga bisani ya sauya masa wajen aiki zuwa ma’aikatar bibiyar ayyuka inda a nan ne ya yi murabus.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana godiyarsa ga Injiniya Diggol bisa ƙoƙari da jajircewarsa da sadaukarwa, da kuma bin ƙa’idojin aiki a lokacin da yake zama ɗan majalisar zartarwa ta jiha.

A cewar sanarwar, Gwamnan ya yi wa Diggol fatan alheri a harkokin da zai sanya a gaba.

Sanarwar dai ba ta bayyana dalilin ajiye aikin da Diggol ya yi ba.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe