Gwamnatin Zamfara Za Ta Kafa Tubalin Bunkasa Ilimi – Dauda Lawal

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na ganin ta kafa tubali mai inganci a harkar ilimi don ’yan baya su samu ilimi mai inganci a Zamfara.

Gwamna Lawal ya bayyana haka ne a ranar Asabar ɗin da ta gabata yayin gasar wasanni na shekara ta 2024 karo na uku na makarantar Almufida International Academy da ke Gusau.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa mai makarantar ya bai wa Gwamna Lawal lambar yabo a matsayin Babban Kwamandan Abokantaka na Kwalejin (GCFC).

Ya ce, Gwamnan ya yaba da yadda ɗaliban suka nuna ƙwazo a lokutan wasanni daban-daban.

A yayin jawabin nasa, Gwamna Lawal ya nuna jin daɗin sa ga yadda makarantar ke gudanar da ayyukanta na ɗora ɗalibai kan kyawawan halaye.

Ya kuma yaba wa ɗaliban bisa kyawawan wasannin motsa jiki, haɗin kai, da kuma ƙwarewar da suka nuna.

“Abin da na gani a nan ya burge ni, waɗannan halaye masu kyau suna nuna kyakkyawar makoma.

“Na zo ne a yau domin nuna goyon baya da nuna ƙwarin gwiwa wajen inganta fannin ilimi a jihar Zamfara. Idan dai za a iya tunawa, na kafa dokar ta-ɓaci a fannin ilimi da lafiya na jihar a wani shiri na gwamnati na.

“Shawarar mayar da martani ga ƙalubalen da harkar ilimi ta Zamfara ke fuskanta, mataki ne mai kyau na ganin ’yan baya sun samu ilimi mai inganci.

“Ilimi shi ne ƙashin bayan kowace al’umma, kuma Zamfara ba za ta iya yin watsi da shi ba.”

Gwamnan ya kuma zagaya, inda ya duba kayayyakin da kwalejin ta ke da su domin bunƙasa ƙwarewar ɗalibai.

Related Posts

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun