Haƙuri Tsakanin Ma’aurata Da Mutuntawa Kan Sa Aure Ya Ɗore -Mustapha Muhammad

Daga Ibrahim Muhammad

An bayyana haƙuri a aure shi ne matakin da yakan sa ya ɗore a sami zaman lafiya, don haka yana da mutuƙar muhimmanci ma’aurata su karrama juna su rika mutunta iyayen juna da ba su daraja Allah zai musu Jagora ya sa albarka a auren.

Babban sakataren yaɗa labarai na Gwamnan jihar Kano, Mustapha Muhammad ne ya bayyana hakan da yake zantawa da ‘yan jarida a ɗaurin auren ‘ya’yan mataimakin Gwamnan jihar Kano, Kwamared Aminu Abdussalam da aka yi a masallacin Alfurƙan ranar Lahadi.

Ya ce an san Mahaifin Amaren da aka ɗaura wa auren Mataimakin Gwamnan jihar Kano, Aminu Abdussalam mutum ne na jama’a mai karrama su da mutunta su. Don haka ba abin mamaki ba ne na ganin irin yawan mutane da suka zo don ɗaurin auren ‘ya’yansa.

Mustapha Muhammad ya yi nuni da cewa duk mutumin da yake karrama mutane suna duba mutuntawa da yake musu a dukkan sha’aninsa su je ballantana kuma shi mataimakin Gwamnan jihar Kano, Kwamared Aminu Abdussalam mutum ne karimi mai kyautatawa duk wanda ya zo kusa da shi.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun