Kwankwaso Jagora Ne Da Ke Da Kishin Bunƙasa Ilimi -Alhaji Gambo Ɗankoli

Daga Ibrahim Muhammad

Abin farin ciki ne mu taya ya’yanmu murna bisa karatu da suka yi har wasu suka fita da sakamako kyakkyawar a wannan jam’ia ta Aliko Ɗangote da jagora sanata Dakta Rabiu Musa Kwankwaso ya kafa .

Alhaji Abdulkadir Gambo Ɗankoli ne ya bayyana hakan da yake zantawa da yan jarida a yayin karrama Kwankwaso da jami’ar kimiyya da fasaha ta Wudil ta yi ya ce suna alfahari da wannan katafaren taro da tun kafuwar jami’ar baya jin an taba taro da mashahuran mutane masu mulki da sarauta da attajirai suka taru don bikin yaye wadannan dalibai da karrama mutane.

Yace wannan abin jin dadi ne Injiniya Dakta Rabiu Musa Kwankwaso shi ya samar da wannan jami’a ta kimiyya da fasaha ta Aliko Dangote saboda kishin talaka da dan talaka.

Alhaji Abdulkadir Gambo Dankoli ya ce suna farin ciki da jin dadi da karramawa da jami’ar ta yiwa Dakta Rabiu Musa Kwankwaso duba da gudummawa da ya bayar na kafa jami’ar ta habaka.

Ya ce da Kwankwaso bai yi tunanin samar da Jami’ar Wudil ba da wannan alherin ba za a same shi ba suna godewa sauran wadanda suke bada gudunmawa wajen haɓakar jami’ar.

Ya kara da cewa Allah ya sakawa jagora tsohon Gwamna, tsohon minista tsohon dan takarar shugabancin kasar nan na NNPP Dakta Rabiu Musa Kwankwaso da alkhari ,wannan gudummawa da ya assasa dama sun sani shi jagora ne kuma jirgi ne wajen gudanar da cigaban ilimi a jihar Kano da Nijeriya gaba daya.

Alhaji Abdukadir Gambo Dankoli ya yi kira ga magoya baya da masu tasowa idan suka sami dama suyi koyi da jagoran Kwankwasiyya yanda ya zo ya kafa jami’o’i guda biyu a jihar Kano bayan makarantu na gaba da Sakandare 24 da ya samar da kuma tura dalibai ya’yan talakawa karatu waje da mafi yawa sun gama suna anfanar da cigaban al’umma.

  • Related Posts

    WOTCOSA Ajin 1975 A Shekara 50: Sun Karrama Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje Da Tagwayen Lambobin Yabo

    Ƙungiyar tsofaffin ɗaliban tsohuwar makarantar horon malamai ta mata ta Kano (WTC), Women Teachers College Old Girls Association (WOTCOSA) da yanzu ake kiran a makarantar da Goverment Girls College (WTC)…

    Ɗaliban Ƙaramar Hukumar Dala Da Gwamnatin Kano Za Ta Tura Manyan Jami’o’i Na Cikin Gida Da Ƙasashen Waje Karatun Digiri Na Biyu, Sun Yi Taron Nuna Godiya

    Daga Ibrahim Muhammad Ɗalibai ‘yan asalin ƙaramar hukumar Dala da za su tafi karatu manyan jami’o’i a ciki da wajen ƙasar nan da gwamnatiin jihar Kano ta ɗauki nauyinsu sun…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun