Me Ya Sa Hukumar tace Finafinai Ta Jihar Kano Ta Dakatar Da Nuna Finafinan Hausa 22 Masu Dogon Zango?

Daga Ibrahim Muhammad

Hukumar tace  finafinai ta jihar Kano ta dakatar da nuna wasu manyan finafinan guda 22 masu dogon zango.

Shugaban Hukumar, Abba El-mustapha ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya raba wa manema labarai.

Ya ce gwamnatin jihar Kano ta ɗauki matakin ne a ƙoƙarinta na tabbatar da ana bin dokar tace finafina sau da ƙafa, tare da ƙara ɗora masana’antar Kannywood a kan turba madaidaiciya.

A cewar sanarwar, “An ɗauki wannan matakin ne biyo bayan tattaunawa da manyan jami’an Hukumar, tare da dogon nazari da aka yi.  domin kawo ƙarshen ƙorafe-ƙorafen da ake yawan karɓa don ƙara inganta ayyukan Hukumar, tare da masana’antar Kannywood”.

Sunayen finafinan da aka dakatar sune:-

1. Dakin Amarya

2. Mashahuri

3. Gidan Sarauta

4. Wasiyya

5. Tawakkaltu

6. Mijina

7. Wani Zamani

8. Labarina

9. Mallaka

10. Kudin Ruwa

11. Boka Ko Malam

12. Wa yasan Gobe

13. Rana Dubu

14. Manyan Mata

15. Fatake

16. Gwarwashi

17. Jamilun Jiddan

18. Shahadar Nabila

19. Daɗin Kowa

20. Tabarma

21. Kishiyata

22. Rigar Aro

Shugaban Hukumar ya ce, doka ce ta ba su damar tace duk wani fim, tare da lura da ayyukan  masana’antar Kannywood matsawar suna da rijista da Hukumar a ko’ina suke. Don haka ya shawarci  masu ɗaukar nauyin  finafinan da su tabbatar da bin wannan doka da  dakatar da saka finafinan a gidajen talabijin da kafar sadarwa.

Haka kuma ana sanar da su cewa su miƙo finafinan ga Hukumar domin tantance su, tare da ba su shaidar inganci ta tacewa nan da mako  ɗaya mai zuwa, wato daga Litinin 19-25, Mayu, 2025, domin gujewa fushin doka.

Hukumar ta nemi haɗin kan dukkannin gidajen talabijin da Hukumar da ke lura da kafafen yaɗa labarai ta ƙasa (NBC), kan su ci gaba da taimaka mata domin samun nasarar abin da ta sa a gaba na tsaftace jihar Kano da masana’antar Kannywood.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun