Ƙaramar Hukumar Ɓagwai Ta Yi Fice A Noma Da Kiwo -Hon. Bello Gadanya

Daga Ibrahim Muhammad

Shugaban ƙaramar hukumar Ɓagwai Hon. Bello Abdullahi Gadanya ya yaba wa Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa Kwamared Aminu Abdussalam bisa shirya taron kalankuwa na nuna al’adu na gargajiya da sana’oi da ake tun kaka da kakanni.

Ya bayyana haka ne da yake zantawa da ‘yan jarida a rumfar ƙaramar hukumar Ɓagwai da suka baje kolin kayayyaki da suke nomawa.

Ya ce sun kawo abin da suke nomawa a yankin da ke da tasiri a noma da kawo abin da suke da su na gargajiya sun baje kolinsu jama’a sun gani.

Shugaban na ƙaramar hukumar na Ɓagwai ya nuni da cewa yankin ya yi fice wajen noma rani da damina, suna da katafaren dam da suke noma kayan lambu da kiwon kifi, ko a ‘yan kwanaki baya ma ya jagoranci zuba jarin kifi a dam ɗin don a samar da kifi mai yawa.

Hon. Bello Abdullahi Gadanya ya ce irin wannan taro na nuna al’adu, mataki ne na inganta kimar al’ummarmu da nuna irin sana’o’i da muka gada muke alfahari da wanzuwarsu har yanzu kuma zai amfanar da matasa masu tasowa.

  • Related Posts

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya damƙa Lambar Karramawa ta Ƙasa a Ayyukan Hidimta wa Al’umma (NEAPS) 2025 ga Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa ayyukan da gwamnati ta gudanar…

    Tsarin Kwankwasiyya Ne Ya Fi Dacewar Da Al’ummar Kano -Injiniya Iliyasu Usman

    Daga Ibrahim Muhammad An bayyana ƙaramar hukumar Nasarawa da ke jihar Kano da cewa suna zaune lafiya babu rigimar siyasa ko wani abu na daban a tsakanin ‘yan Kwankwasiyya, jagorancinsu…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?