Ɓata-Gari Sun Auka Wa Mutane Bayan Rabon Kayan Tallafi Da Ɗan Majalisar Tarayya Ya Yi A Kano

Daga Ibrahim Muhammad

Wasu gungun ɓata-garin matasa sun yi yunƙurin ƙwace kayayyaki da wayoyin al’umma bayan rabon tallafi da ɗan majalisar tarayya na Fagge Muhammad Bello Shehu ya yi a gidan gwamnati.

Shaidun gani da ido a lokacin da abin ke faruwa sun ce gungun wasu matasa ne a bakin gidan gwamnatin suka far wa mutane suna yunƙurin ƙwacen waya da kayan da aka bai wa wasu da suka amfana daga tallafin.

Wata majiya ta ce yawancin ɓata-garin matasan ba ‘yan ƙaramar hukumar Fagge ba ne, wasu gungun haɗakar ɓata-gari ne daga wasu ƙananan hukumomin ƙwaryar birni da suka haɗu a yayin taron raba tallafin suka shiga ƙwacen.

Ɗaukin gaggawa da jami’an tsaro suka kawo suka tarwatsa gungun matasan ya bayar da kariya ga al’umma.

Mutane da dama sun yi kira a. kan lallai a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki na zaƙulo ɓata-garin matasan da hukunta su domin hana faruwar hakan a gaba.

Wani da muka tattauna da shi kan lamarin ya ce, ya zama dole gwamnati ta ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki a kai, duba da cewa a kusa da gidan gwamnati da ake da tsaro an far wa mutane da ƙwace a taron raba tallafi, idan za a yi a wani waje daban za a iya fuskantar barazana makamancin wannan muddin ba a ɗauki mataki ba.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History