Sabon Ajiyan Kano Ya Yi Alƙawarin Ci Gaba Da Hidimta Wa Al’umma

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Ajiyar Kano Sarkin Fulanin Shanono, Alhaji Ja’afar Muhammad Shanono ya ce za su ci gaba da ba da gudunmawa kamar yadda ya saba a mahaifarsa ta ƙaramar hukumar Shanono wajen hidimta wa jama’a ta fanninn ci gaban Ilimi, kiwon lafiya, ruwan sha da sauran abubuwa tun kafin wannan naɗin.

Ya bayyana hakan ne da yake zantawa da ‘yan jarida bayan naɗin da Sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi ll ya yi masa a fadarsa a matsayin sabon Ajiyar Kano.

Ya ce shi ba shi da ta cewa sai godiya ga Sarkin Kano Khalifan Tijjaniya Muhammad Sanusi saboda dawo musu da wannan sarautar tasu da ta daɗe ba ta gidansu, amma ya zama sababin dawowarta gidan.

Alhaji Ja’afar Muhammad Shanono ya ce halayyarsa masu nagarta da Sarki ya bayyana ya san su ne saboda yi aiki da Maimartaba Sarki Muhammad Sanusi tun yana Gwamnan babban bankin ƙasa a matsayin mataimakinsa na musamman tsawon shekaru biyar har a halin yanzu kuma shi yana ci gaba da yi wa ƙasa hidima a bankin na ƙasa.

Ajiyar Kano Sarkin Fulanin Shanono, Alhaji Ja’afar Muhammad Shanono ya bayyana godiya ga jama’a bisa irin dafifi da suka yi na taya shi murna wanda soyayya ce ta kawo hakan wanda Allah ya yi wa arziƙin mutane sai ya gode wa Allah.

Ajiyar na Kamo ya jaddada godiya ga Allah da masarautar Kano ƙarƙashin jagorancin Sarki Malam Muhammad Sanusi ta yi da hakimai da duk sauran jama’a da suka zo don taya shi murna.

Ita ma ɗaya daga cikin ƙanne shakikai ga sabon Ajiyar Kano da aka naɗa, Hajiya Hadiza Magaji Buhari ta ce, suna farin ciki mutuƙa da godiya ga Sarkin Muhammad Sanusi da wannan karamci da dama da ya yi masu.

Ta ƙara da cewa su sun san Ajiyan Kano mutum ne da yake abubuwa da dama na taimaka al’umma, duk wanda yake shiga Shanono zai ga ɗimbin ayyukansa, kama daga samar da ruwan sha, makarantu, taimaka wa mata da marayu da sauran fannoni ba kawai a Shanono kaɗai ba da sauran wurare.

Hajiya Hadiza Magaji Buhari ta ce tana da tabbacin ɗan’uwan nata zai ci gaba da hidima da yake ga al’umma, kuma tana bai wa al’ummar Shanono tabbacin sun sami ɗa mai mutunci da kishi na ci gabansu.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun