An Raba Wa Mata 200 Jari A Fagge, Kano

Daga Ibrahim Muhammad

Mata 200 a ƙaramar hukumar Fagge kowacce ta sami jari na ₦50,000 da Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya sahale a raba musu.

Taron rabon da aka gudanar a harabar sakatariyar ƙaramar hukumar Fagge da shugaban ƙaramar hukumar ya jagoranci bayarwa ya sami halartar sakataren mulki na ƙaramar hukuma Aliyu Tijjani Sanata da zaɓaɓɓun kansuloli sauran masu ruwa da tsaki.

A jawabinsa yayin bikin ƙaddamar da tallafin, shugaban ƙaramar hukumar Hon.Salisu Usman Masu
ya ce, sun tsaya sun yi wannan aiki na rabon tallafi ne da ya jagoranta saboda bin umurnin Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya gaya musu lallai wannan abu ya tafi ƙasa saboda a lokacin yaƙin neman zaɓe ya yi alƙawarin in Allah ya ƙaddara shi ne Gwamna za a taimaki mata da jari.

Ya ce wannan cika alƙawarin ne ɗaya ɗauka wannan kuma ba shi ne na farko ba, an yi na ɗaya da na biyu da na uku. Wannan shi ne na huɗu. “Mun tsaya mu yi aikin ne da kanmu domin mu tabbatar da cewa an yi abin da ya kamata. Allah shi ne shaida, kuma al’umma ma shaida ne duk mazaɓar da muka kirawo akwai jagororanta da kansila da sauran masu ruwa da tsaki a gabansu aka yi komai, kuma abin ya tafi hannun wanda ya kamata,” in ji shi.

Hon. Salisu Masu ya ja hankalin matan da suka amfana da tallafin da cewa kar wani ya zo ya ce zai karɓi wani abu daga wurinta. “Wannan shi ne saƙon Gwamna. Abu ya tafi hannun mata da suka zaɓe mu. Abin da muka yi yana tabbatar wa al’umma da Gwamna ya yi rabon cikin gaskiya da riƙon amana,” ya tabbatar.

Masu ya yi kira ga mata da suka sami wannan tallafi na ₦50,000 su yi amfani da shi yadda ya kamata ‘, “Domin a lokacin Kwankwaso an ba da irin tallafi makamancin wannan, har yanzu a mazaɓa ta akwai mata da za su nuna maka wani abu na tallafi da aka ba su tun wancan lokacin.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun