Da Gwamnati Za Ta Haɗa Kai Da Kamfanonin Taki Na Gida Za A Sami Nasarar Tallafi A Take Wa Manoma -MD. Abfullahi Rara

Daga Ibrahim Muhammad

Shugaban kamfanin taki na Rara Agrovet, MD. Alhaji Abdullahi Rara ya bayyana cewa harkar noma yana tafiya daidai a jihar Jigawa sakamakon gwamnati ta na bakin ƙoƙarinta sannan kamfanoni na waje na gida irin nasu sun shigo suna taimaka wa manoma.

Ya ce kusan kowane gari a lungu da saƙo na cikin jihar babu inda ba sa ba su tallafi da taimako na taki idan sun gama noma su biya a ko’ina sun shiga suna taimaka wa manoma ba domin manoma suna samun irin wannan taimakon daga gare su ba, da wahalar da za a shiga da ƙarancin taki da sai ya ci musu tuwo a ƙwarya.

Ya yi nuni da cewa a ɓangaren gwamnati ana samun matsala na idan ta bai wa manoma tallafi na rancen kayan noma, amma a ƙi dawo da shi, an yi shiri na ƙungiyoyin manoma da tsare-tsare daban-daban na gwamnati, amma ba su ɗore ba sakamakon ba a dawowa da bashin da ake ba su.

Amma ya ce su a nasu tsarin na kamfanoni na cikin gida da suke taimakon manoma a jihar Jigawa suna da tsare-tsare da gwamnati ba su da shi, su sun tsara da lauyoyin su da sauran duk wani mai ruwa da tsaki sun tsara abin da zai tafi daidai sun zauna da su, kuma komai yana tafiya yadda ya kamata ba su fiya samun matsaloli ba.

MD. Alhaji Abdullahi Rara ya ce ita gwamnati a tsare-tsaren ta ba ta neman kamfanoni, ƙalubalen da take samu na rashin neman kamfanoni ne a ciki da za ta nemi kamfanoni su shigo da su za su sami nasara wajen tsara yadda za a tallafa wa manoma sauƙin samun taki da yadda za su biya, amma sai gwamnatin suna yin abin ne da ka shi ya sa abin da ake bai wa manoma ba ya dawowa.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History