Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo mutum ne mai karamci -Dr Faruq Umar Abubakar, Magatakardan Hukumar Lura Da Aikin Jinya Da Unguwanzoma ta Nijeriya

 

Daga Ali Kakaki
Magatakardan Hukumar Lura Da Aikin jinya da Unguwanzoma na Nigeriya Dr Faruq ya yi wannan furucin ne a yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan da kammala bikin rantsar da daliban da suka yi karatun jinya daga kasashe daban-daban na duniya. Karo na Goma sha Daya, (11) wanda aka Gudanar a Dakin taro na jamiar maryam Abacha Amerikan University dake birnin kano,
Sannan har wala yau ya kuma bayyana Farfesa Gwarzo da cewa mutum ne mai karamci, domin ya karrama su kuma sun gani a aikace; “ya karrama mu ya mutunta mu, duk abin da ake yi ma bako a faranta masa ya yi mana. Kuma tsare-tsaren da aka yi, babu bambanci da cewa taron da aka yi a Abuja ne aka yi shi”.
Ya ce za su rika kai taron rantsar da dalibai sassa daban-daban na kasar, kuma yadda suka ga taron na bana a Jami’ar Maryam Abacha American University, sun yaba matuka.
Ya kuma yi kira ga daliban da su ji tsoron Allah; “aikin nan da kuka yi karatu domin shi ku gudanar da shi ta yadda su al’umma za su bambance ma’aikacin jinya da wanda ba na jinya ba. Amfanin ilimi ka kawo canji. Al’umma na da korafi ga ma’aikatan jinya, ilimi shi zai kawo canji. Ku yi amfani da wannan basirar ilimin da kuka samu domin kawo canji ga al’umma kan matsayin yadda suke yi wa ma’aikatan jinya kallo”, ya jaddada.
Dr. Faruq ya ce akwai bukatar daliban su sauya tunanin al’umma domin su fahimci cewa aikin jinya aiki ne na kawarai da kuma taimakon al’umma da kawo ci gaba ga mara lafiya.

Related Posts

Bincike Ya Tabbatar Ƙungiyar Da Ta Zargi Gwamna Lawal Da Yi Wa ’Yan Bindiga Afuwa Ta Bogi Ce

An gano cewa zargin da ake yaɗawa cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi afuwa tare da sakin ‘yan bindiga da aka yanke wa hukunci ba shi da tushe…

WOTCOSA Ajin 1975 A Shekara 50: Sun Karrama Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje Da Tagwayen Lambobin Yabo

Ƙungiyar tsofaffin ɗaliban tsohuwar makarantar horon malamai ta mata ta Kano (WTC), Women Teachers College Old Girls Association (WOTCOSA) da yanzu ake kiran a makarantar da Goverment Girls College (WTC)…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History