Ɗan Masanin Ƙauran Namoda Sahabi Liman Zai Gina Makarantar Nazarin Addinin Musulunci

Daga Ibrahim Muhammad

A ƙoƙarinsa na kishin bunƙasa ilimin addinin Musulunci, Ɗan Masanin Ƙauran Namoda, Alhaji Sahabi Usman zai gina katafariyar babbar makaranta ta nazarin ilimin addini da aka sa wa suna Sahabi Liman Academy a garin na Ƙauran Namoda da ke jihar Zamfara.

Za a gudanar da taron aza tubalin gina cibiyar ne a harabar filin da ke a ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda.

Wannan tasa mutane da dama suke nuna mutuƙar farin ciki da jin daɗinsu ga wannan babban abin alkhairi daya kawo wa yankin.

Da ma akwai ma ginin katafaren masallacin Juma’a da Alhaji Sahabi Liman yake ginawa da zai ɗauki yawan masallata 12,000 idan aka kammala shi.

Mutane da dama da muka zanta da su sun bayyana cewa wannan aikin na alkhari dama Ɗan Masanin na Ƙauran Namoda, Alhaji Sahabi Liman ya saba aiwatarwa domin mutum ne da kullum yake kyautatawa cigaban al’umma.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?