NUPSRAW Ta Cira Wa Gwamnatin Kano Hula

Daga Ibrahim Muhammad

Kwamared Yahaya Yakub Umar Shugaban ƙungiyar ma’aikata sakatarori da masu aikin kwamfuta da masu ɗauko rahoto na ma’aikatan gwamnati na jihar Kano, ya cire wa gwamnatin Abba Kabir Yusuf a kan yadda take kula da ma’aikata.

Kwamared Umar ya bayyana cewa, Ranar Ma’aikata, rana ce da Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware domin tunawa da ma’aikata.

Ya ce a kasar nan a jihar Kano aka fara shi lokacin Gwamna Abubakar Rimi har ƙasar ta ɗauka gaba ɗaya. Don haka Kano ta fi kowa alfahari da farin ciki rana da za ma’aikata za su fito su bayyana matsaloli da buƙatunsu da kuma godiya ga shugabanni.

Shugaban ƙungiyar NUPSRAW ya bayyana gamsuwa da irin kulawar da gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin Abba Kabir Yusuf take bai wa ma’aikata tun daga zuwanta ta zama abokiyar ma’aikata ta irin alkhairai da suke da yawa na kyautata masu da suka haɗa da biyan kuɗaɗen ma’aikata da suka yi ritaya garatuti da suke bi bashi da biyan karin kudin mafi ƙarancin albashi da aka zartar da wuri da kuma biyan albashi kafin ƙarshen wata ga ma’aikata da sauran abubuwa da dama.

Kwamared Yahaya Yakub Umar ya yi kira ga Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf a kan ya cigaba da biyan kuɗaɗen garatuti da ya soma biya na sama da kashi 30, yanzu suna fata daga nan zuwa shekara ɗaya kamar yadda ya yi alƙawari Allah ya sa su ga ya gama biyan kuɗin gaba ɗaya.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun