‘Yan sandan Sun Gano Gawar Budurwa Ba Kai A Cikin Otal A Adamawa

Daga Hadi Bawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa na ci gaba da bin diddigin wani mutum da ake zargi da aikata tsafi bayan wani mummunan kisa da aka yi wa wata budurwa a cikin wani otel da ke karamar hukumar Yola ta Arewa a ranar 18 ga watan Janairu.

An dai yi zargin cewa wani mutum ne da suka shigo otal din tare ya kashe shi tare da yanke masa kai kuma ya arce.

Wanda ake zargin ya bayyana wa masu una da otal don cewa zai je ya yi siyayya, daga nan bai sake dawo ba. Bayan binciken dakin wanda ake zargin, ma’aikatan otal din sun gano gawar budurwar mara kai.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Afolabi Babatola, cikin gaggawa ya ba da umarnin a gudanar da bincike domin kamo wanda ya aikata wannan aika-aika da duk wani mai hannu a cikin wannan danyen aikin domin gurfanar da shi gaban Kuliya.

Rundunar ‘yan sandan ta jaddada muhimmancin hada kai da sauran jami’an tsaro don kare rayukan ‘yan kasa da kuma tabbatar da tsaron lafiyarsu da dukiyarsu.

Kazalika rundunar ta bukaci jama’a su kwantar da hankalinsu, tare da ba su tabbacin cewa dukkanin hukumomin tsaro suna aiki tare domin kamowa da gurfanar da wanda ake zargi da aikata laifin a gaban kotu.

  • Related Posts

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    By: Okoi Obono-OblaSome people in Cross River State, seeing the passion and intensity with which I canvass the plight of Mrs. Theresa Akwaji Ushie—the embittered Chairman of Bekwarra Local Government…

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    By: Godwin Onuh Odeh Distant and contemporary history is replete with instances of state failure. This is not limited to Africa’s Ghana empire, Mali, Songhai, Oyo empire, Kanem Bornu, Bini…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History