Akwai Kyakkyawan Zumunci Tsakanin Masarautar Haɗejia Da Ta Kano -Yariman Magajin Rafin Haɗejia

Daga Ibrahim Muhammad Kano

An bayyana cewa akwai daɗaɗɗiyar kyakkyawar alaƙa da ‘yan’uwantaka da zumunta tun na kaka da kakanni a tsakanin masarautar Haɗejia da ta Kano har yanzu kuma suke a tare.

Alhaji Muhammad Inuwa Babandede Yariman Magajin Rafin Haɗejia ne ya bayyana hakan da yake zantawa da ‘yan jarida a lokacin ya halarci bikin naɗin da Sarki Muhammad Sanusi II ya yi wa ɗansa a matsayin Chiroman Kano.

Ya ce wannan zumunci zai ci gaba da wanzuwa da kyautata alaƙa tsakanin masarautun biyu domin nasarar hidimta wa al’umma da kare martabar addinin Musulunci da kuma kyawawan al’adu.

Yariman Magajin Rafin Haɗejia Alhaji Muhammad Inuwa Babandede ya yi kira ga sabon Chiroman na Kano DSP Aminu Sanusi ya yi koyi da irin hali na karamci da mutuntawa da Sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi yake da su da son cigaban jama’a.

Yariman Magajin Rafin Haɗejia ya bayyana mutuƙar murnarsa ga naɗin da aka yi wa sabon Chiroman na Kano da yi wa dukkan baƙi da suka halarci naɗin fatan alkahiri da fatan komawa gidajensu lafiya.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?