Abba Kabir Yusuf Gwamnan Ma’aikata Ne Da Talakawa -Shugaban NULGE, Kano

Daga Ibrahim Muhammad

An bayyana cewa a dukkan Nijeriya idan aka ce wane ne Gwamnan ma’aikata, ba kawai ma’aikatan jihar Kano na faɗin ƙasar nan ma, za su ce Abba Kabir Yusuf ne.

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi na ƙasa reshen jihar Kano, Kwamared Ibrahim Muhammad ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida.

Ya ce duk abin da Gwamnan jihar Kano zai yi domin jin daɗin ma’aikata tun daga zuwan sa yana yi, musamman a mataikin jiha da na ƙananan hukumomi ya zo yana biyan basusukan na fansho da ya zo ya tarar ba a biya ba.

Ya yi nuni da cewa su a ƙananan hukumomin da sauran ma’aikata daga ranar da aka ce an yi ƙarin albashi na N70 ,000 shi Gwamna Abba Kabir Yusuf bai tsaya a haka ba, sai da ya ƙara ma a kai, kuma ya biya a kan lokaci ba tare da wata matsala ba.

Ya ce su abin da yake ci masu tuwo a ƙwarya shi ne na Hukumar ma’aikata na ƙananan hukumomi, kuma yanzu Gwamna ya faɗa ya yi Hukumar nan, ya samar mata da wuri wanda za ta fara aiki. Kuma yana sahalewa ma’aikata bukatunsu.

Kwamared Ibrahim Muhammad ya ce ƙungiyarsu ta NULGE mai son cigaba ce, duk abin da zai kawo mata nasara a cikin al’amuranta shi suka sa a gaba. Shi ya sa suke samun nasara na samun kofi a taron ranar ma’aikata, shi ya sa ma sun ɗauki kofi a taron bukin ranar ma’aikata ta duniya, kuma za su cigaba da ɗauka a gaba.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun