Abubakar Ɗangambo Ya Zama Sabon Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Jarida Na Yanar Gizo

Daga Ibrahim Muhammad

An rantsar da sabbin shugabannin ƙungiyar ‘yan jarida na yanar gizo reshen jihar Kano.

Taron an gudanar da shi ne a sakatariyar ƙungiyar ‘yan jarida ta ƙasa reshen jihar Kano.

Shugaban kwamitin ƙaddamar da ƙungiyar, Alhaji Ahmad Aminu, ya buƙaci ‘yan jarida na yanar gizo su riƙa tantance gaskiyar labarai kafin wallafawa domin kauce wa yaɗa labaran ƙarya da kan iya haifar da rikici.

Sabon shugaban ƙungiyar, Kwamared Abubakar Ɗangambo, ya bayyana ƙudurinsa na haɗa kai da sauran ‘yan ƙungiyar domin kare martabar aikin jarida da kuma tallafawa cigaban jihar Kano.

Ya ce za su yi aiki tuƙuru wajen tabbatar da sahihancin bayanai da wayar da kan al’umma cikin gaskiya da riƙon amana.

Sauran sabbin shugabannin da aka rantsar sun haɗa da Khadijah Aminu a matsayin mataimakiyar Shugaba, Isyaku Ahmad a matsayin Sakatare. Zahara’u Nasir a matsayin mataimakiyar sakatariya, Abbas Yusha’u a matsayin Ma’ajin Kuɗi, da Zainab Bello a matsayin mataimakiyar Ma’aji.

Taron rantsarwar ya samu halartar ‘yan jarida da dama daga faɗin jihar Kano.

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya taya Abubakar Abdulkadir Ɗangambo murna bisa zabensa da aka yi a matsayin Shugaban ƙungiyar.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Litinin.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce kafa wannan sabon reshe na kafafen yaɗa labarai ta yanar gizo, ƙarƙashin ƙungiyar ‘yan jarida na jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Kwamared Sulaiman Dederi, zai taka rawa wajen tallafa wa kafafen yaɗa labarai wajen tabbatar da gaskiya da adalci a rahotanni.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da goyon bayan duk wani ƙoƙari da zai inganta harkar yaɗa labarai da kuma ƙarfafa haɗin kan ‘yan jarida domin ci gaban jihar Kano.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun