AMBALIYAR RUWA: GWAMNAN ZAMFARA YA JAJANTA WA GWAMNATIN BORNO, YA BA DA GUDUNMAWAR MILIYAN N100 GA WAƊANDA ABIN YA SHAFA

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jajanta wa gwamnati da al’ummar Jihar Borno sakamakon mummunar ambaliyar ruwa da ta afku a Maiduguri.

A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne wata tawaga ƙarƙashin jagorancin Mallam Abubakar Nakwada, Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, ta wakilci gwamnan a Maiduguri.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa maƙasudin ziyarar ita ce jajanta wa Gwamnatin Borno da al’ummar jihar kan ambaliyar ruwa mai ratsa zuciya.

Yayin da yake miƙa saƙon jaje na Gwamna Lawal a fadar gwamnatin jihar Borno, Mallam Abubakar Nakwada ya sanar da gudunmawar Naira Miliyan 100 da gwamnatin jihar Zamfara ta bayar a matsayin nuna goyon baya da tallafawa.

Ya ce, “A madadin jama’a da gwamnatin jihar Zamfara, ina rubutu domin nuna alhininmu game da mummunar ambaliyar ruwa da ta afku sakamakon ballewar ruwa daga madatsar ruwa ta Alu da ke Maiduguri.

“Muna matuƙar baƙin ciki da rahotannin da ke cewa sama da mutum miliyan ɗaya ne suka rasa muhallansu sakamakon wannan ibtila’i.

“Lamarin wannan ibtila’i yana ratsa zuciya. Al’ummar jihar Zamfara – waɗanda suka fuskanci irin wannan ibtila’i, duk da cewa bai kai na Borno ba – suna yi wa ‘yan uwansu maza da mata a yankunan abin ya shafa addu’ar ‘Allah Ya mayar da alkhairi, Ya kuma kiyaye faruwar hakan a nan gaba’, yayin da suke cikin wannan mawuyacin hali. Muna roƙon Allah Ta’ala ya jiƙan waɗanda suka rasa rayukansu, ya kuma mayar wa waɗanda suka rasa dukiyoyinsu da mafificin alkhairi.

“A matsayin nuna goyon baya da tallafawa, gwamnatin jihar Zamfara na bayar da gudunmawar zunzurutun kuɗi Naira Miliyan 100,000 domin gudanar da ayyukan agaji da kuma taimaka wa al’ummomin da abin ya shafa a Maiduguri.

“Muna roƙon Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya ci gaba da taimakon waɗanda abin ya shafa, ya ba su ƙarfin gwiwa da juriya wajen sake gina rayuwarsu.

Related Posts

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal