An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

Daga Ibrahim Muhammad

An buɗe masallacin ’yan nama da ke harabar Kasuwar Muhammad Abubakar Rimi (Kasuwar Sabon Gari), wanda ƙungiyar mahauta ta sabunta gininsa, tare da mayar da shi na zamani.

Babban Malami, Sheikh Ibrahim Khalil ne ya jagoranci Sallar Azahar a masallacin, tare da bayyana aikin a matsayin aiki na alheri, inda ya ja hankalin al’umma kan tsaftar masallaci, tare da yin alƙawarin bayar da gudunmawar Naira 50,000.

Manajan Daraktan Hukumar kasuwar, Hon. Abdul Bashir Hussaini, ya bayyana masallaci a matsayin gidan Allah, yana mai jaddada cewa duk wanda ya taimaka wajen gina shi zai samu lada mai yawa.

Ya kuma yaba wa ƙungiyar mahauta bisa haɗin kai da rawar da suka taka.

Tsohon shugaban hukumar kasuwar, Alhaji Sa’id Dattijo Adahama, da shugabannin ƙungiyar mahauta sun bayyana farin cikinsu kan sabunta masallacin da aka gina shekaru da dama da suka gabata.

Mai zanen ginin masallacin, Arc. Binta Ahmad, ta yaba da haɗin kai da biyayyar ’yan nama, tare da bayyana shirin ɗora bene domin ƙara faɗaɗa masallacin a nan gaba.

Shugabanni da ’ya’yan ƙungiyar mahauta sun gode wa Hukumar kasuwa da ɗaiɗaikun mutane bisa gudunmawar da suka bayar, suna mai tabbatar da aniyar cigaba da inganta masallacin domin amfanin al’umma.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History