An dawo da wutar lantarki ga Radio Nijeriya Kaduna

Hukumar Lantarki ta kasa ta dawo da wuta ga Radio Nijeriya Kaduna kwana guda bayan yanke wutar ba zato ba tsammani.

Shugaban Radio Nijeriya Kaduna Malam Buhari Auwalu, yace wannan dai ya biyo bayan naminijin kokarin Ministan yada labarai Alhaji Mohammed Idris Malagi da shugaban hukumar gidajen Radio Tarayya Dr. Muhammad Bulama

Malam Buhari Auwalu yayi bayanin cewa, ministan yada labarai ya bada muhimmiyar gudummuwa wajen aikin da hukumomin da suka dace ganin an karshen wannan matsala

Malam Buhari Auwaku yace Ganin irin gudummuwar da Radio Nijeriya Kaduna ke badawa wajen fadakarda al’umma ne yasa shugaban hukunar gidajen Radion Tarayya Dr. Bulama Mohammad da Minista suka yunkuro wajen tallafawa Radio Kaduna domin tabbatar da ba a Sami katsewar shirye shirye ba.

Daukar matakin gaggawa da kyakkwan tsari tare da aiki da hukumomin da suka dace sun taimaka gaya wajen maganin wannan matsala nan take.

Daga dai wannan yunkuri, Radio Kaduna da ya fi kowane Radio dadewa Yana bada gudummuwa a Arewa, zai ci gaba da aikin sa kamar yadda aka sanshi a cewa Malam Buhari Auwalu..

Yusuf Zubairu

Related Posts

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano