An Kafa Dokar Taƙaita Zirga-Zirgar Babura A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya amince, tare da sanya hannu a dokar taƙaita zirga-zirgar babura a jihar Zamfara.

A Alhamis ɗin nan ne gwamnan ya rattaba hannun a fadar gwamnatin jihar da ke Gusau.

A cikin wata sanarwa da Kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa Majalisar tsaro ta jihar ne ta yanke shawarar taƙaita zirga-zirgar baburan, a wani taron gaggawa da suka gudanar ranar Laraba.

Sulaiman Bala ya ce, don ganin an aiwatar da wannan doka, Antoni Janar na jihar, Abdul’aziz Sani SAN ne ya gabatar wa da gwamnan dokar mai lamba No. 07, 2024, inda kuma ya amince da ita.

“A yau, Gwamna Dauda Lawal ya rattaba hannu a dokar taƙaitawa, tare da haramta zirga-zirgar babura daga ƙarfe 8 na dare zuwa ƙarfe 6 na safe a duk faɗin jihar Zamfara.

“An yi wannan doka ne a ƙoƙarin da ake yi na kare rayuka da dukiyar jama’a, a kuma rage ayyukan ta’addanci da ya addabi jama’a, da kuma ƙarfafa wa ƙoƙarin gwamnati na maganin rashin tsaro a jihar.

“Saboda haka, daga yanzu an haramta zirga-zirgar babura gaba ɗaya daga ƙarfe 8 na dare zuwa ƙarfe 6 na safe a duk faɗin jihar.

“Babu wani babur da aka amincewa ya hau titi a jihar nan a tsakanin waɗannan awoyi da aka ambata. An ba jami’an tsaro izinin kama duk wanda ya karya wannan doka.

“An baiwa Antoni Janar na jihar Zamfara damar ya hukunta duk wanda aka kama ya keta wannan doka.”

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?