Daga
Ibrahim Muhammad
Gamayyar matasa masu kishin samar da cigaban ƙaramar hukumar Rimin Gado sun yi zama da Shugaban ƙaramar hukumar, Hon. Muhammad Sani Salisu Jili domin fahimtar juna da yadda za a ciyar da yankin gaba.
Wannan ya biyo bayan janye zanga-zangar lumana da matasan suka shirya yi kan matsalolin da ake fuskanta a yankin da suka haɗa da na matsalar ruwa da makarantu da asibitoci.
A yayin ganawar tasu, Shugaban ƙaramar hukumar na Rimin Gado, Hon. Jili ya ce, za su yi bakin ƙoƙarinsu wajen samar da ruwa da kyautata makarantu da asibitoci don kyautata harkar ilimi da lafiyar al’ummar yankin.
Sani Salisu Jill ya ce, gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin Alhaji Abba Kabir Yusuf ta amince da ɗaga likkafar asibitin Rimin Gado zuwa babba da faɗaɗa dam domin samar da wadataccen ruwan sha da inganta ɓangaren cigaban ilimi domin ko a kasafin kuɗi gwamnatin Kano ta fi ba ɓangaren ilimi fifiko.
Shi ma a nasa ɓangaren Shugaban matasan masu fafutukar kawo gyara da cigaban Rimin Gado, Salim Muhammad Mudassir ya ce sun zauna da shugaban ƙaramar hukumar sun sami daidaito da fahimtar juna, kuma za su ba su lokaci, kuma sun ce a je a kalli yadda yanayin asibiti, makarantu da samar da ruwa yake da kuma sanar da su tsare-tsaren da ake na gyara su.
Ya yaba da kyakkyawan haɗin kan da shugaban ƙaramar hukumar ya ba su. Ya shaida musu tsare-tsarensa, sun kuma ba shi shawarwari da suke fata nan da ɗan ƙanƙanin lokaci za a sami sauƙi a matsaloli da yake damun al’ummar yankin.






