Askarawan Zamfara Sun Kashe Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

Gwamnatin Jihar Zamfara ta tabbatar da kisan riƙaƙƙen ɗan bindiga, Kachalla Ɗanbokolo da ya addabi wasu yankunan jihar.

Mai Bai Wa Gwamnan Jihar Shawara Kan Harkokin Tsaro, Ahmad Manga ya bayyana kisan Ɗanbokolo a matsayin gagarumin nasara a yaƙi da matsalar tsaro.

”Ɗanbokolo mutum ne da ya fi Bello Turji fitina, ya fi Turji aikata miyagun laifuka, illa kawai shi Turji sunansa da ya karaɗe kafofin yaɗa labarai”, inji Ahmad Manga.

”Mutanensa da aka kashe sun haura 100, saboda haka wannan gagarumar nasara ce a gare mu”, inji shi.

Kacalla Ɗanbokolo ya rasa ransa ne a wata arangama a ƙauyen Kurya, tsakanin Askarawan Zamadara na gwamnatin jihar Zamfara da mayaƙan ɗan bindigar.

Ana kallon mutuwar Ɗanbokolo – wanda ake ganin a matsayin ubangidan Bello Turji – a matsayin ci gaba a ɓangaren yaƙi da ‘yan bindiga.

Ɗanbokolo ya shafe shekaru masu yawa yana kai hare-hare yankunan jihar Zamfara tare da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

Riƙaƙƙen ɗan bindigar ya gamu da ajalinsa ne tare da wasu ɗimbin mayaƙansa a lokacin da Askarawan Zamfara – da gwamnatin jihar Zamfara ta samar.

Mazauna yankin na kallonsa a matsayin mutum marar imani da tausayi da ya addabi yankunansu, ta hanyar kai hare-hare da kisan mutane.

Related Posts

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History