Assasa Farfaɗo Da Al’adun Gargajiya; Gwamnatin Kano Ta Yi Abu Mai Kyau -Hon. Tukur Muhammad Wada

Daga Ibrahim Muhammad Kano

An bayyana assasa farfaɗo da al’adunmu na gargajiya da ware ranaku na musamman a jihar Kano a matsayin wani muhimmin abu, kuma abin alfahari ne da farin ciki da gwamnatin jihar Kano ta yi.

Shugaban ƙaramar hukumar Rano Hon. Tukur Muhammad Wada ne ya bayyana hakan a yayin da yake zantawa da manema labarai a rumfar da suka baje koli a wajen taron farfaɗo da al’adu da aka yi a Kano.

Ya ƙara da cewa kamar masarautarsu ta Rano suna da kyakkyawan tarihi na sarauta da zamantakewa da sana’o’i da suka yi fice a kai, “Don haka muna murna da wannan taro na farfaɗo da al’adu,” in ji shi.

Ya ce su ma a matakin ƙaramar hukumar Rano za su cigaba da assasa al’adun gargajiya ta hanyar fito da abubuwa da ba a sani ba na al’adun al’umma, domin na baya su sani su riƙe su yi alfahari da su.

Hon. Tukur Muhammad Wada ya yi kira ga al’ummar Rano da ma jihar Kano baki ɗaya a kan su san cewa riƙo da kyawawan bal’adu da suka gada yana da muhimmanci, kuma zai ƙara musu kima a idon duniya muddin suka riƙe su da kyau.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?