Aure Na Buƙatar Haƙuri Da Mutunta Juna -Hon. Abdullahi Yahaya Tsamiyar Kara

Daga Ibrahim Muhammad

An yi kira ga ma’aurata musamman su zama masu girmama juna da sanin ya kamata da yin haƙuri a tsakaninsu.

Ɗan Malisar jihar Kano mai wakiltar ƙaramar hukumar Gezawa, Hon. Abdullahi Yahaya Tsamiyar Kara ne ya yi kiran a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida bayan ɗaura auren ‘yarsa Ubaidah Abdullahi Yahaya da Angonta Zayyanu da aka yi a babban masallacin Juma’a na garin Tsamiyar Kara bayan idar da Sallah.

Ya yi nuni da cewa shi aure muhimmin ibada ne, kuma Sunnah ce ta koyi ga Manzon Allah ga al’ummar Musulmi, kuma mutuntaka ce ga dukkan ɗan’adam, don haka abu ne mai muhimmanci ma’aurata su zama masu darajanta juna da girmamawa a tsakanin su.

Hon. Abdullahi Yahaya Tsamiyar Kara ya jaddada cewa ta hanyar aure ne ake samum kyakkyawar zuriya da ake fatan ta zama ta gari da za su tashi da kyakyawar tarbiyya da iyaye za su raine su a kai, dan haka ma’aurata su yi ƙoƙarin gina kyakkyawar zamantakewa a tsakaninsu da zai naso a kan zuriyarsu.

Ɗan majalisar dokokin na jihar Kano mai wakitar Ƙaramar hukumar Gezawa, Hon. Yahaya ya gode wa ɗimbin al’umma da suka haɗa Hakimi da shugaban jam’iyyar APC na Gazawa da ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban da jami’an tsaro da iyayen ƙasa da sauran al’umma bisa halartar ɗaurin auren.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History