Ban Rubuta Wa Wata Jam’iyya Wasiƙar Neman Iznin Shiga Ba

Daga Ibrahim Muhammad

Sanata Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso ya musanta labarin da ake yaɗawa na cewa ya rubuta wa jam’iyyar APC buƙatar shiga cikin ta.

A rana Slhamis ne aka yi ta yaɗa labarin har aka ce hakan ne dalilin da ya sa masu ruwa da tsakin jam’iyyar APC na jihar Kano suka gudanar da wani taron gaggawa a Abuja.

A cikin wata sanarwa da Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso ya fitar da safiyar ranar Juma’a ya ce labarin ba shi da tushe balle makama.

“An wayi gari da yaɗa jita-jita a kafafen sada zumunta cewa mun gabatar da takardar nuna sha’awar shiga wata jam’iyyar siyasa a ƙasar nan”, n ji Kwankwaso.

Ya fito fili ya nesanta kansa daga wannan batu, da ya bayyana cewa, “ba mu taɓa miƙa irin wannan takarda ga kowacce jam’iyya ba'”.

Sanarwar Jagoran Kwankwasiyya jigon jam’iyyar NNPP na ƙasa ya ce yana shawartar jama’a da su ci gaba da bibiyar sahihan hanyoyin da aka tanada ta ofishinsa domin samun ingantattun bayanai game da abubuwa da ya sa a gaba.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?