Barazanar Kawo Hari Da Trump Ya Yi: Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Wa Matsayar Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso

Daga Ibrahim Muhammad

Gwamnatin Tarayya ta nuna mutuƙar jin daɗin ta ga Madugun Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso tare da gode masa bisa kishin ƙasa da ya nuna na mayar da martani ga maganganu da shugaban Amurka ya yi Trump na barazanar yiwuwar kawowa Nijeriya hari

Mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana matsayar Kwankwaso abu ne da ya dace dukkan shugabannin siyasa su yi ba tare da la’akari da jam’iyya ba, su haɗa kai su tsaya waje ɗaya don kare ƙasarmu a matsayin ‘yan ƙasa na gari.

Ya bayyana matsayar Kwankwaso a matsayin ta kishin ƙasa, yana kira ga sauran shugabannin jam’iyyun adawa su bar siyasa a gefe, su tsaya tsayin daka wajen kare martabar ƙasar nan a gaban abin da ya kira “ɗaukacin ƙalubalen waje.”

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a shafiinsa na X ya yi Allah wadai da matsayar Trump na kiran ƙasar nan mai damuwa ta musamman bisa zargi mara tushen na cewa ana yi wa mabiya addinin Kirista kisan gilla.

Tsohon Gwamnan na jihar Kano, wanda ya yi wa jam’iyyar NNPP takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 ya yi gargadin cewa maganar Donald Trump na iya tayar da hatsaniyar addini da ta’azzarar matsalar tsaro a ƙasar nan, kuma ya yi jan hankali ga shugaban na Amurka maimakon wannan kamata ya yi ya tallafa wa ƙasar wajen kawar da matsalar barazanar tsaro.

  • Related Posts

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya damƙa Lambar Karramawa ta Ƙasa a Ayyukan Hidimta wa Al’umma (NEAPS) 2025 ga Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa ayyukan da gwamnati ta gudanar…

    Tsarin Kwankwasiyya Ne Ya Fi Dacewar Da Al’ummar Kano -Injiniya Iliyasu Usman

    Daga Ibrahim Muhammad An bayyana ƙaramar hukumar Nasarawa da ke jihar Kano da cewa suna zaune lafiya babu rigimar siyasa ko wani abu na daban a tsakanin ‘yan Kwankwasiyya, jagorancinsu…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?