Dauda Lawal Zai Mai Da Babbar Tashar Motar Gusau Ta Zamani

A taron majalisar zartarwar jihar, wanda ya gudana Talatar nan a fadar gwamnatin jihar da ke Gusau, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da gina babbar tashar mota irin ta zamani a garin Gusau a wani ɓangare na aikin sabunta birane a Jihar.

A ranar Talatar nan ne gwamnan ya jagoranci taron Majalisar Zartarwa na musamman da shugabannin Jihar Zamfara a gidan gwamnati da ke Gusau.

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, a cikin watar sanarwar da ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa majalisar ta tattauna muhimman batutuwa da za su amfanar da Jihar Zamfara.

A cewarsa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gina tashar mota ta zamani ga kamfanin Fieldmark Construction Ltd, wanda adadin kuɗinsa ya kai Naira 4,854,135,954.53.

Aikin gina wannan tashar, wani muhimmin ɓangare ne na shirin sabunta birane a jihar, kuma zai inganta hanyoyin sufuri da sauƙaƙa rayuwa a jihar.

Ma’aikatar Kula da Ƙananan Hukumomi da Ma’aikatar Kasuwanci, Masana’antu da Yawon Buɗe Ido ne za su ɗauki nauyin aikin tare, yayin da Ma’aikatar Ayyuka da Samar da Ababen More Rayuwa za ta sa ido a kan yadda za a gudanar da aikin.

Tuni Ma’aikatar Ayyuka ta tsara tare da samar da wani ƙudiri na cikin gida don gudanar da aikin tare da miƙa shi ga Ofishin Kula da Harkokin Ƙasa da Ƙasa na jihar, wanda bai kushe komai ba game da wannan ƙudiri.

Babbar tashar ajiye motoci ta zamanin ta ƙunshi abubuwa da dama kamar; gina ofisoshin gwamnati da ƙungiyoyi, kafa ofishin kashe gobara, gina masaukin baƙi, samar da asibiti, kafa ofishin ‘yan sanda, ƙirƙirar ɗakin ajiye kaya, samar wurin POS, da kafa garejin gyaran mota da wurin wankin mota.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?