Gidauniyar Abdullahi Rara Za Ta Raba Kayan Abinci Da Na Sa Wa Ga Marayu Sama Da 2000 A Hadejia A Ramadan

Daga Ibrahim Muhammad

Kamar yanldda aka saba, sama da marayu 2000 ne a garin Haɗejia za su amfana da kayan abinci da na Sallah da Gidauniyar Abdullahi Rara ta za ta raba.

Shugaban Gidauniyar, Alhaji Abdullahi Rara ne ya bayyana hakan a wajen tantance waɗanda za su amfana da tallafin.

Ya ce kamar yadda suka saba taimaka wa marayu da yi musu ɗinki da sauran hidindimu da suke yi, bana ma sun soma shirye-shirye a kai.

Ya ce, “Wannan karon ma Allah ya kawo mu. Dama mukan soma shirye-shirye ne daf da shigowar watan Azumin Ramadan, mu kira teloli maza da mata sama da 30 mu ba su ɗinkunan yara marayu su yi,” in ji shi.

Ya yi nuni da cewa zai kai har cikin Azumi ana ɗinka kayan a ƙarshen kwanakin Azumi ranar 27 suke fara rabon kayan ga har zuwa ragowar kwanakin Azumi har bayan Sallah.

Alhaji Abdulahi Rara ya yi kira ga masu hali a cikin al’umma a kan su riƙa tallafa wa marayu da masu ƙaramin ƙarfi a cikin al’umma domin rabauta a duniya da lahira.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?