Gwamnan Zamfara Ya Ziyarci Wuraren Da Ambaliyar Ta Shafa A Gummi

A ranar Asabar ne Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya gudanar da ziyarar gani da ido zuwa yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa a Ƙaramar Hukumar Gummi ta Jihar.

A makon da ya gabata ne mamakon ruwan sama ya haifar da ambaliya a wasu yankunan ƙaramar hukumar Gummi, inda ya lalata gidaje da dama.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce tawagar gwamna Lawal ta fara ne da gaisuwar ban girma ga fadar Mai Martaba Sarkin Gummi, Mai Shari’a Lawal Hassan.

A cewar sanarwar, gwamnan ya zagaya garin Gummi ne domin jajanta wa waɗanda ambaliyar ruwan ta shafa kafin ya wuce garin Gayari domin duba irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

Gwamna Lawal ya nuna matuƙar damuwa bayan duba irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

Ya ƙara da cewe, tuni tawagar injiniyoyi suka fara bincike a yankunan domin samun mafita mai ɗorewa.

“A yau, na zo ƙaramar hukumar Gummi ne domin yin jaje tare da gudanar da ziyarar gani da ido a yankunan da ambaliyar ruwa ta shafa a makon jiya.

“Nan da nan bayan na samu labarin faruwar lamarin, sai na aika kwamishinoni biyu domin su kai ziyara kuma su jajanta wa al’ummomin da abin ya shafa.

“Bayan ziyarar mataimakin gwamna, na tura tawagar injiniyoyi domin su duba tare da sanin musabbabin ambaliyar ruwa.

“Yana da muhimmanci a lura cewa na ba da umarnin a fara aiki nan take don daƙile faruwar irin wannna matsalar a nan gaba.

“Ina so in yi amfani da wannan dama wajen sanar da ku cewa na bayar da gudunmawar buhunan abinci guda 10,000 da suka haɗa da shinkafa, masara, da gero, domin raba wa waɗanda ambaliyar ruwan ta shafa. Yanzu haka manyan motocin na kan hanyar Gummi domin a raba wa al’umma.

“Ni kuma a madadin gwamnatin jihar Zamfara, ina tallafa wa waɗanda abin ya shafa da Naira Miliyan 100. Bugu da ƙari, duk waɗanda abin ya shafa, za a raba musu filaye nesa da yankin da ke da haɗari domin su gina sabbin gidaje.”

Related Posts

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Daga Ibrahim Muhammad Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Dakta Rahila Aliyu Muktar, ta cimma ɗimbin nasarori a cikin shekaru biyu na shugabancinta. Hukumar ta ƙuduri…

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko