Hon. Muhammad Hassan Ya Gode Wa Al’ummar Da Suka Halarci Ɗaurin Auren ‘Ya’yansa

Daga Ibrahim Muhammad

Ɗimbin al’umma ne daga sassa daban-daban suka halarci ɗaurin auren ‘ya’yan Kwamishina na ɗaya a Hukumar Amintttattu na Asusun Fansho na jihar Kano, Hon. Hassan Muhammad Amin a unguwar Chiranchi a yankin ƙaramar hukumar Gwale, Kano a safiyar ranar Asabar.

Hon.Hassan Muhammad Amin, wanda ya ba da auren ‘ya’yansa mata guda biyu; Amarya Halima Hassan Muhammad Amin (Sadiya) da angonta Umar Shitu Sharubutu da Amarya Saudat Hassan Aminu (Yesmin) da Angonta Injiniya Mahmud Amin.

Uban Amaren Hon. Hassan ya bayyana matuƙar jin daɗi da godiya ga Allah da ɗimbin mutane da suka amsa wannan gayyata tasa ta zuwa ɗaurin auren na ‘ya’yansa, wanda ƙauna ce ta jawo hakan.

Ya bayyana aure da cewa ibada mai muhimmanci, Sunna ce ta Manzon Allah da idan aka yi shi ana buƙatar haƙuri da fahimta da girmamawa da sanin ya kamata a tsaƙanin ma’auratan, da hakan zai zama wani ginshiƙi na samar da zuriyya mai cike da kyakkyawar tarbiyya.

Hon. Hassan Muhammad Amin, ya gode wa ma’aikatan Hukumar Amintttattu na Asusun Fansho ƙarƙashin jagorancin Alhaji Habu Muhammad Fagge, wanda suka sami halartar ɗaurin auren da waɗanda suka yi masa addu’a da fatan alkhairi daga nesa.

Haka kuma ya gode wa muƙarraban gwamnatin jihar Kano da ‘yan siyasa da ‘yan kasuwa da ma’aikata da sauran al’umma maza da mata da ‘yan’uwa da abokan arziƙi da suka zo suka taya shi farin cika a wannan hidima, tare da yin addu’ar Allah ya saka wa kowa da alheri.

Mutane da dama a yayin ɗaurin auren sun bayyana cewa ba su yi mamakin irin yawan mutanen da suka halarci ɗaurin aure ba bisa la’akari da halin Hon. Hassan Muhammad Amin mutum ne mai karamci, taimako da girmama mutane.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

    Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

    Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

    Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko