Kano Ce Kan Gaba A Samun Nasarar Cin Jarabawar NECO

Daga Ibrahim Muhammad

Jihar Kano ta fito a matsayin jiha ta fi kowa cin jarabawar kammala Sakandare ta cikin gida (SSCE Internal) ta shekarar 2025 wacce Hukumar Jarabawa ta Ƙasa (NECO) ta gudanar.

Wannan gagarumar nasara ta samo asali ne daga manyan gyare-gyaren da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gudanar tare da ci gaba da inganta ilimi.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba.

Sanarwar ta ce, Shugaban NECO, Farfesa Ibrahim Wushishi, ya bayyana cewa daga cikin ɗalibai 1,358,339 da suka zauna jarabawar a Yuni/Julai, ɗalibai 818,492, wanda yake daidai da kashi 60.26 cikin 100, sun samu darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi.

Haka kuma, ɗalibai 1,144,496, wanda yake daidai da kashi 84.26 cikin 100, sun samu darussa biyar da suka wuce, ba tare da la’akari da waɗannan darussa biyu ba.

Kano ce ta jagoranci ƙasa da ɗalibai 68,159 (kashi 5.020 cikin 100 na jimillar ɗaliban ƙasa) suka samu darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi. Lagos ta biyo baya da ɗalibai 67,007 (kashi 4.930 cikin 100), yayin da Oyo ta zo ta uku da ɗalibai 48,742.

Wannan nasarar tarihi ta nuna sakamakon shugabancin Gwamna Abba Kabir Yusuf mai kishin ilimi, wanda a koyaushe ya sanya kuɗi, gina makarantu, da kuma bunƙasa samun damar ilimi a sahun gaba cikin ayyukan gwamnatinsa.

A cikin kasafin kuɗin 2024 da 2025, ɓangaren ilimi ne ya samu kaso mafi tsoka, abin da ya bai wa gwamnatin damar gudanar da manyan gyare-gyare da suka farfaɗo da makarantu, tare da mayar da ƙarfin gwiwa ga ilimi a matsayin muhimmin ɓangaren da gwamnati ke bai wa muhimmanci.

  • Related Posts

    WOTCOSA Ajin 1975 A Shekara 50: Sun Karrama Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje Da Tagwayen Lambobin Yabo

    Ƙungiyar tsofaffin ɗaliban tsohuwar makarantar horon malamai ta mata ta Kano (WTC), Women Teachers College Old Girls Association (WOTCOSA) da yanzu ake kiran a makarantar da Goverment Girls College (WTC)…

    Ɗaliban Ƙaramar Hukumar Dala Da Gwamnatin Kano Za Ta Tura Manyan Jami’o’i Na Cikin Gida Da Ƙasashen Waje Karatun Digiri Na Biyu, Sun Yi Taron Nuna Godiya

    Daga Ibrahim Muhammad Ɗalibai ‘yan asalin ƙaramar hukumar Dala da za su tafi karatu manyan jami’o’i a ciki da wajen ƙasar nan da gwamnatiin jihar Kano ta ɗauki nauyinsu sun…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?