Karancin Mai Ya Kara Ta’azzara A Sakkwato, Lita Ta Haura 2,000

Al’ummar jihar Sakkwato na ci gaba da fuskantar kunci saboda tsananin karancin man fetur da ya addabi yankin.

An dai samu cikas a harkokin kasuwanci, inda ’yan kasuwar bayan fage ke sai da man daga Naira 2,000 zuwa 2,500 kan kowace lita, kamar yadda jaridar Neptune Prime ta ruwaito.

Wasu mazauna garin sun yi kira ga gwamnati da ta sa baki don shawo kan lamarin don kada abubuwa su kara tabarbarewa.

Sun ce lamarin ya fara shafar harkokin kasuwanci tare da jawo wa mutane wahala saboda farashin man fetur din a wajen ‘yan bumburutu ya kai Naira 2,500 kan kowace lita.

A halin da ake ciki, Kamfanin Mai na Nijeriya (NNPC Ltd) ya dora alhakin dogayen layukan motocin da ake gani a Legas, Abuja da sauran jihohin tarayyar kasar kan matsalolin kayan aiki da suka samu.

Kamfanin, ya ce an warware matsalolin, kuma nan ba da jimawa ba komai zai koma daidai.

“Kamfanin NNPC Ltd yana son ya fayyace cewa tsananin da aka shiga na karancin man fetur da ake gani a halin yanzu a wasu yankuna a fadin kasar nan ya samo asali ne sakamakon matsalar kayan aiki, kuma tuni an shawo kan su,” in ji sanarwar.

Har ila yau, kamfanin ya nanata cewa har yanzu farashin man fetur bai canza ba.

NNPCPL ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano