Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wanda Ya Kashe Kwarton Matarsa

Wata babbar kotu a jihar Ekiti a yankin Ado Ekiti ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wani matashi mai shekara 28 bisa samun sa da laifin kashe wani mutum da yake zargin yana lalata da matarsa.

Kamar yadda jaridar PUNCH ta ruwaito, kotun ta yanke wa Ayodeji Alomoge hukuncin kisa ta hanyar ratayewa bayan ta same shi da laifin kisan kai.

“A ranar 21 ga watan Yuni, 2022, a Ikere Ekiti, Alomoge ya kashe wani da ake kira Ogunleye Ayomide, hakan ya saba wa sashe na 234 na dokar laifuka ta jihar Ekiti, 2021.” in ji Mai Shari’a Jubril Aladejana.

Mahaifin marigayin, Ige Ogunleye, a cikin bayanin da ya yi wa ‘yan sanda, ya ce an yi masa waya cewa dansa (marigayin), Alomoge da abokansa sun yi masa dukan tsiya. “Na garzaya zuwa wurin, na iske dana a cikin wani hali, an ji masa raunuka iri-iri a kansa da bakinsa.

“Na kuma iske Alomoge tare da wasu mutane. Na tambaye shi dalilin daukar matakin da ya dauka, sai ya ce Ayomide ya dade yana hulda da matarsa, kuma ya gargade shi da ya daina, ko kuma ya kashe shi.

“Na dauki Ayomide zuwa wani asibiti da ke kusa, daga baya kuma na kai shi asibitin koyarwa na Jami’ar Ilorin, jihar Kwara, inda daga baya ya rasu,” Ogunleye ya kara da cewa.

Mai gabatar da kara, Kunle-Shina Adeyemo, ya gabatar da shaidu biyar, tare da gabatar da bayanan wanda ake tuhuma, da hotunan marigayin, da kuma rahoton Likita na musabbabin mutuwar a matsayin shaida, kuma kotu ta yi la’akari da su.

Wanda ake tuhumar ya yi magana ne ta bakin lauyansa, Adeyinka Opaleke, inda ya roki kotun da ta yi wa wanda yake karuwa adalci da jin kai, tare da la’akari da abin da ya fusata shi ya dau matakin da ya dauka.

A hukuncin da kotun ta yanke a ranar Alhamis, Mai shari’a Jubril Aladejana ya ce, “Bisa hujjojin da suka bayyana a gare shi, wanda ake kara ya dauki matakin da ya dauka ne sakamakon kishi, kuma bai bi matakan da doka ta tanada ba wajen huce haushinsa.

Saboda haka na sami wanda ake tuhuma da laifin kisan kai da ake yi masa. Don haka aka yanke masa hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Alkalin ya ba da umarnin cewa: “Za a rataye Ayodeji Alomoge a wuyansa har sai ya mutu.”

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano