Makarantu Masu Zaman Kansu Suna Mutuƙar Ba Da Gudunmawa Wajen Cigaban Ilimi -Injiniya Aminu Aliyu

Daga Ibrahim Muhammad

An bayyana makarantu masu zaman kansu suna mutuƙar bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban ilimi domin gwamnati kaɗai ba za ta iya gamsar da ba da ilimi ga al’umma gaba ɗaya ba, musamman a matakin farko na Firamare da ƙaramar Sakandire ba.

Tsohon Kwamishinan Ayyuka Gidaje da Sufuri
na juhar Kano, Hon. Aminu Aliyu Wadil ne ya bayyana hakan a taron yaye ɗalibai da raba kyautuka na makarantar ‘Yan Dutse.

Ya ce dole makarantu masu zaman kansu ne za su cike wannnan giɓin, kuma gwamnatoci sun ba da yanayi mai kyau ga makarantun, su ma makarantu masu zaman kansu sun karɓi ƙalubalen da gwamnati ta yi musu ana samun cigaba, duk da dai ba a rasa ‘yan abubuwa na ƙalubale, amma akwai Hukuma ta musamman da take kula da sa ido ga makarantun don kiyaye doka da tarbiyya don a sami ingantaccen ilimi.

Hon. Injiniya Aminu Aliyu Wadil ya ce a matsayinsa na ɗan ƙasa yana ganin ƙoƙarin da Majalisun Ƙasa suke na yin doka na lallai duk ma’aikatun gwamnati sai sun sanya ‘ya’yansu a makarantun gwamnati yana ganin hakan ya faru ne saboda taɓarɓarewar makarantu mallakar gwamnati.

Tsohon Kwamishina a jihar Kano, Hon. Amin Aliyu Wadil ya bayyana cewa makarantar ‘yan Dutse koyaushe tana yaye ɗalibai managarta domin yana da yara guda shida a makarantar, wasu sun gama suna Jami’a, wasu har sun yi aure.

Hon. Injiniya Aminu Aliyu Wadil ya yadda makarantar ke shirya taron yaye ɗalibai da raba kyautuka, wannan ya nuna irin ƙoƙarin iyaye da ƙwazon malamai shi ya sa ma suka zo makarantar don halartar wannan taro don gamsuwa da abubuwa da ake.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano