Nijar ta zargi ECOWAS da rashin kyakkyawar manufa akanta

Firaministan Nijar Ali Mahaman Lemine Zeine, ya ce kungiyar kasashe Afirka ta Yamma ECOWAS ko kuma CEDEAO sam ‘’ ba ta kyakkyawar manufa’’ zuwa ga kasar ta Nijar.

A wannan alhamis ne ya kamata tawagar kungiyar da kuma wakilin Togo da ke matsayin kasa mai shiga tsakani sun kasance a birnin Yamai don tattaunawa da gwamnatin mulkin sojin kasar, amma sai aka wayi gari tawagar ta Ecowas ta kaurace wa taron.

A zantawarsa da manem alabarai a gaban ministan harkokin wajen Togo Robert Dussey, Lemine Zeine ya ce rashin kasancewar tawagar Ecowas a wannan haduwa ta ranar alhamis, alama ce da ke tabbatar wa duniya cewa kungiyar ba ta bukatar tattaunawa, sannan kuma tana rawa ne da bazar wasu kasashe amma ba kare manufofin al’ummar Yankin yammacin Afirka.

A cewar firaministan na Nijar, da farko tawagar Ecowas ta ce ta gaza zuwa Yamai ne saboda jirginta bai samu izinin da ke ba shi damar ratsa sararin samaniya da kuma sauka a kasar ba, zargin da firaministan ya musanta.

Tun ranar 26 ga watan Yulin bara, lokacin da sojoji suka kifar da zababbiyar gwmanati da ke karkashin jagorancin Mohamed Bazoum, kungiyar ta Yammacin Afirka ta sanya wa kasar takunkuman karya tattalin arziki da kuma rufe iyakoki, tare da neman sake dawo da kasar ta Nijar kan turbar dimukuradiyya.

To sai dai yayin da aka gaza samun fahintar juna tsakanin sojojin da suka kwaci mulki karkashin jagorancin Janar Abdourahmane Tchiani da kuma Ecowas, Togo, daya daga cikin kasashe mambobi a kungiyar ta yi gabatar da shirin shiga tsakani wanda bangarorin biyu suka amince da shi.

Related Posts

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano