Rasuwar Galadiman Kano: An Rasa Bango Abin Jingina -Bala Gwagwarwa

Daga Ibrahim Muhammad

An bayyana rasuwar Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi da cewa wani bango ne, kuma majingini na addini da kuma masarauta aka rasa.

Tsohon ma’ajin jam’iyyar APC na ƙasa, kuma tsohon shugaban ƙaramar hukumar, Nasarawa tsohon Kwamishina, tsohon ɗan takarar Gwamnan jihar Kano a zaɓen 2023 a jam’iyyar SDP, Alhaji Bala Muhammad Gwagwarwa ne ya bayyana hakan.

Ya ce daga irin halayya da ya kamata a koya daga Galadiman akwai haƙuri, “Saboda ba za ka taɓa jin maganarsa a kan dukkan wasu al’amura ba, ko kuma ya ɗauki ɓangaranci shi ya sa ma, idan aka lura a lokacin da aka yi jana’izarsa ta haɗa dukkannin ɓangarori na babu wani maganar bambanci.

Ya ƙara da yin nuni da cewa hatta cece-kace da ake yi akan masarautar Kano sai ta sarara saboda kowa na Galadima ne. Saboda haka wani bango ne aka rasa a jihar Kano ta yau,” in ji shi.

Alhaji Bala Muhammad Gwagwarmaya ya roƙi Allah ya maye gurbinsa da makamancinsa, “Irin haƙuri da yake idan duk aka tsaya a kai za a tarar da alkhairi,” ya jaddada.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?