Riƙo Da Al’adunmu Masu Kyau Na Da Muhimmanci Sosai -Hon. Salisu Bebeji

Daga Ibrahim Muhammad

An bayyana al’adunmu da cewa na da muhimmanci sosai suna ajiye tarihi da ɗabi’u masu kyau da tarbiyya da rayuwa ta addini da usulinmu.

Hon. Dakta Alhassan Salisu Bebeji shugaban ƙaramar hukumar Bebeji ne ya bayyana hakan ya ce rana da gwamnatin jihar Kano ta ware na musamman ta nunin al’adun gargajiya na iyaye da kakanni da aka gada abu ne mai muhimmanci.

Ya ce, “Shi ya sa irin kyawawan al’adunmu, mu cigaba da koyi da su, domin suna tsare yaranmu daga shiga abubuwa na Turawa da abubuwa da ba su kamata ba saboda al’adunmu sun nuna mana yanayi mai kyau.”

Shugaban na ƙaramar hukumar Bebeji ya ƙara da cewa shi ya sa Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf yake ba da dama da kulawa wajen kyautata al’adunmu da addini da kula da tsaro, lafiya da zamantakewa kuma ya bai wa ƙananan hukumomi 44 dama ta kyautata al’adu da zamantakewa.

Ya ce ƙaramar hukumarsa ta Bebeji ta shahara a harkar noma da samar da abinci ba da bunƙasa tattalin arziƙi ana alfahari da ita a jihar Kano ko lokacin Dalar gyaɗa sun ba da gudunmawa saboda ta shahara a noman gyaɗa, masara da sauran kayan abinci.

Dakta Alhassan Salisu Bebeji ya ce suna daga ƙananan hukumomi da suke bunƙasa tattalin arziƙi, saboda noma da kiwo da suke, kuma gwamnatin Kano tana ba su tallafi na taki da kayan noma don inganta noma. “Don haka mun ba da tallafin taki kyauta da maganin fashi da jari ga manoma. Domin haka Bebeji ta zama daga wacce ke bunƙasa tattalin arziƙin jihar Kano da Nijeriya wajen samar da abinci da walwalar al’umma,” ya ƙarƙare.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?