Shugaba Tinubu Ya Taya Gwamna Dauda Lawal Murnar Cika Shekaru 60 Da Haihuwa

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal murnar cika shekaru 60 a duniya.

Shugaba Tinubu ya yaba wa Gwamnan bisa jajircewar sa na ci gaban jihar Zamfara da kuma jajircewar sa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar 2 ga Satumba, 2025

Yayin da yake ba Gwamna Lawal tabbacin ci gaba da goyon bayan gwamnatin tarayya, shugaban ya ƙara ƙarfafa masa gwiwa da ya jajirce wajen ganin an samar da shugabanci na gari, da samar da haɗin kai, da samar da ci gaba mai ɗorewa a jihar.

“Gwamna Dauda Lawal, a madadin gwamnati da al’ummar Nijeriya, ina yi maka fatan samun ƙarin lafiya, ƙarfin gwiwa da hikima yayin da ka ke ci gaba da yi wa al’ummar Jihar Zamfara da ƙasa hidima,” inji Shugaba Tinubu.

  • Related Posts

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun