Tsoro Da Ƙwadayi Ke Sa Wasu ‘Yan Siyasa Ke Rige-Rigen Komawa APC -Ambasada Salga

Daga Wakilinmu

Jigo a jam’iyyar PDP, kuma tsohon ɗan takarar Majalisar Tarayya na ƙaramar hukumar Dala a jihar Kano a 2023, Hon. Ambassador Abdurahman M. Salga, ya nuna matuƙar takaicinsa da rashin kishin al’umma da wasu ‘yan ƙasar nan suke nunawa, musamman ‘yan siyasa daga jihar Kano da a halin yanzu suke sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

Ambassador Abdurahman M. Salga, wanda shi ne shugaban ƙungiyar PDP Iyali Ɗaya, ya yi nuni da cewa son rai da rashin kishi da tsoro da ƙwadayi suka sa wasu ‘yan siyasa daga jihar Kano ke sauya sheƙa daga jam’iyyarsu suna komawa jam’iyyar APC .

Salga ya yi nuni da cewa jam’iyyar APC a mulkin da take na shugabancin ƙasar nan na baya ƙarƙashin Buhari da na yanzu da ake ciki ƙarƙashin Bola Ahmad Tinubu, babu abin da take sai gallaza wa al’ummar ƙasa da azabtar da su.

“Ta sa su cikin mawuyacin halin da ake ciki, amma wasu ‘yan siyasa suna komawa APC .

Hon Ambassada Abdurahman M. Salga, wanda kuma yana ɗaya daga cikin masu goyon bayan tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, ya ja hankali ga matasa maza da mata da sauran al’umma su tashi tsaye kada su kuskura su sake zaɓar duk wani ɗan siyasa da ya koma jam’iyyar APC da a kullum babu abin da take sai gallaza wa al’ummar ƙasar nan tun zuwan ta mulki.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History