Tumburkai Ne Zai Yi Wa PDP Takarar Shugaban Ƙaramar Hukumar Dandume, Katsina

A ranar Laraba, 15 ga Mayu, 2024, Abdullahi Usman Tumburkai ya yi nasarar lashe zaben fid da gwani na takarar shugabancin karamar hukumar Dandume a jihar Katsina da ke tafe a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.

Wata sanarwa da mataimaki na musamman a fannin yada labarai na kwamitin yakin neman zaben, Yusuf Aliyu ya sanya wa hannu, ya tabbatar da cewa an gudanar da zaben ne cikin kwanciyar hankali da lumana.

Abdullahi ya bayyana matukar jin dadinsa game da irin goyon bayan da aka ba shi, inda ya ce: “Ina matukar godiya da kaskantar da kai bisa amincewar da ‘ya’yan jam’iyyarmu suka ba ni. Wannan nasara ta nuna kwazo da sadaukarwar duk wanda ke da ruwa da tsaki a cikin lamarin yakinmu.”

A duk lokacin yakin neman zaben na fid da gwani, Abdullahi ya yi la’akar da muhimman batutuwa da jama’ar yankin ke fuskanta da suka hada da rashin tsaro, ilimi, kiwon lafiya, da kuma ci gaban aikin gona, inda ya sha alwashin magance wadannan matsalolin da ke damun su idan aka zabe shi.

A matsayin dan takarar jam’iyyar PDP, Abdullahi Usman Tumburkai ya himmatu wajen wakiltar bukatun dukkanin mazabun, tare da yin alkawarin yin aiki tukuru domin ganin an samu sauyi mai ma’ana a karamar hukumar Dandume.

Nasarar da aka samu a zaben fid da gwani cikin lalama, ya nuna goyon bayan da Abdullahi Usman Tumburkai yake da shi a tsakanin jama’a, ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki na jama’iyyar PDP, tare da nuna sha’awar da mutane suka nuna a kan takarar tasa, in ji sanarwar.

Abdullahi, wanda kwararren dan jarida ne, ya nuna karfin gwiwar da yake da ita na lashe babban zaben da ke tafe da za a gudanar da shi a shekara 2025, tare da tsaya tsayin daka a kan kudirinsa na magance matsalar rashin tsaro, inganta ilimi, da kula da harkokin kiwon lafiya domin amfanin dukkan mazauna yankin.

Ya jinjina wa irin goyon baya da karfafa gwiwa da yake samu daga magoya bayan jam’iyyar PDP a yankin da ‘yan mazabarsa, tare da fitattun jama’ar yankin da suka hada da Hon. Abdulaziz Tijjani Dandume, Alhaji Ubale Dandume, Alhaji Danfoloti Dandume, Hon. Hamisu Garkuwa, da shugaban jam’iyyar na karamar hukumar Alhaji Danlami Dandume.

  • Related Posts

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

    Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History