Wajibi Ne Ma’aurata Su Zama Masu Biyayya, Haƙuri Da Girmama Juna -Hon. Muhammad Bello Butu-Butu

Daga Ibrahim Muhammad

Ɗan majalisa mai wakilar ƙananan hukumomin Rimi Gado da Tofa, mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Hon. Muhsmmad Bello Butu-Butu, ya yi kira ga ma’aurata ango da amarya su zama masu biyayya da girmama juna, “Domin shi aure ibada ne sunnar Annabi. Mata su bi mazajensu sau da ƙafa a kan kowane umurni da bai saɓa wa shari’a ba,” ya nusar da su.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi jim kaɗan da kammala ɗaurin auren ‘ya’yansa da aka yi a masallacin Rijiyar Zaki a makon jiya, ya ce da babba da yaro da jami’an gwamnati da wakilan Gwamnan Kano da mataimakinsa da ‘yan majalisu na jihar Kano da waɗanda suka zo daga wajenta da wanda suka yi fatan alkhairi daga nesa ya ji daɗi, ya yi farin ciki da yi wa Allah godiya bisa wannan karamci da aka nuna masa.

Hon. Muhammad Bello Butu-Butu ya ce, a matsayinsu na ‘yan siyasa kullum tarbiyya da suke yi wa ‘yan siyasa irin wadda suka gada ce, ta yin biyayya da huƙuri, gaskiya da riƙon amana da yin aiki tuƙuru a duk matsayin da mutum ya sami kansa.

Mataimakin shugaban majalisar dokokin na jihar Kano ya gode wa al’ummar mazaɓar da yake wakilta na Rimin Gado da Tofa a majalisar Kano bisa irin goyon baya da suke ba shi a kowane lokaci. “A ci gada da ta ya mu da addu’ar ydda za mu cigaba da jajircewa wajen sauke nauyin wakilci da kuka ɗora mana,” ya jaddada.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?