Wani DPO a Nijeriya yaki karbar naira miliyan guda daga dan ta’adda

Wani jami’in ‘Yan sanda a Najeriya dake kula da shiyar Tafa a Jihar Kaduna yaki karbar cin hanci naira miliyan guda daga wani shugaban ‘yan ta’addan da ya kama, wadanda suka hana jama’ar jihohin Kaduna, Neja da kuma Zamfara zaman lafiya.

Kakakin rundunar ‘Yan sanda jihar, Manir Hassan ya ce, DPO’n garin na Tafa ya jagoranci tawagar jami’ansa wajen kama ‘dan ta’addan Bello Muhammad da ya fito daga Zamfara a wani otel dake garin tare da samun sa da kudin da ya kai kusan naira miliyan biyu da rabi da ake zargin kudin fansa ne daga garkuwa da mutane.

Hassan yace yayin bincike, Muhammad ya amsa cewar shi mai garkuwa da mutane ne dake gudanar da ayyukansa a dajin Kagarko dake Jihar Kaduna, kuma kudin dake tare da shi wani kaso ne daga cikin kudin fansar da suka karba.

Jami’in yace a cikin wayarsa an gano hotunansa dauke da bindiga kirar AK47 wanda ‘yan sandan suka kwace, abinda ya sa ya yi tayín bada naira miliyan guda ga DPO’s domin kubutar da kansa, amma baturen ‘yan sandan yaki.

Kwamishinan ‘Yan sandan jihar Kaduna, A. D. Ali ya jinjinawa DPO’n da jami’ansa saboda kokarin da suka yi da kuma kin karbar cin hancin.

  • Related Posts

    Bincike Ya Tabbatar Ƙungiyar Da Ta Zargi Gwamna Lawal Da Yi Wa ’Yan Bindiga Afuwa Ta Bogi Ce

    An gano cewa zargin da ake yaɗawa cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi afuwa tare da sakin ‘yan bindiga da aka yanke wa hukunci ba shi da tushe…

    Gidauniyar Abba Aliyu Gandu Ta Raba Solar Ga Al’umma

    Gidauniyar Tallafawa Al’umma ta Abba Aliyu Gandu da ke jihar Kano ta bada horo sana’o’in hannu tare da raba tallafin Solar ga al’umma 500. Wannan shi ne karo ba adadi…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano