Yahaya Bello Ya Sake Fadawa Sabuwar Tsomomuwa

Daga Hadi Bawa

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta ba da umarnin janye dukkan jami’an tsaron da ke gadin tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello.

A ranar Alhamis ne hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon-kasa (EFCC) ta bayyana Bello, a matsayin wanda take nema ruwa a jallo bisa zargin almundahanar Naira biliyan 80.

Fitaccen Lauyan nan da ke Legas, Femi Falana (SAN) ya yi watsi da ikirarin da tsohon gwamnan ya yi na cewa ba za a iya kama shi ba saboda umarnin da wata babbar kotun jihar Kogi ta bayar.

Sufeto Janar na ‘yan sanda Kayode Egbetokun ya ba da umarnin janye dukkan jami’an ‘yan sandan da ke da alaka da tsohon gwamnan ta hanyar sakon da ya aika wa jami’ansa.

Takardar mai lamba: “CB:4001/DOPS/PMF/FHQ/ABJ/VOL.48/34 ta ce: “IG ya ba da umarnin janye dukkan ‘yan sandan da ke da alaka da mai girma tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello.

“Ku yi aiki da wannan umarnin, kuma ku kula da shi don hakan Yana da matuƙar mahimmanci,” in ji shi.

Ita Hukumar shige da fice ta kasa (NIS) a ranar Alhamis din da ta gabata ta sanya Bello a cikin jerin sunayen mutanen da ke sanya wa ido, abin da zai sa a hana shi kasashen ketare.

NIS ta ce; “Sun yi haka ne saboda Bello na fuskantar shari’a a babbar kotun tarayya Abuja” kan badakalar kudaden haram da sauran laifuka.

Takardar, wacce aka rabawa Daraktocin Hukumar Tsaro ta farin kaya (DSS) da Hukumar Leken Asiri ta Najeriya (NIA) da Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda, ta bukaci hukumomin tsaro su kama Bello a duk inda ya suka gan shi a fadin kasar nan.

Babban Lauyan Tarayya Lateef Fagbemi ya bukaci Bello da ya mika kansa girma da arziki.

Ba a dai san inda yake ba har yanzu, yayin da gwamnatin Jihar Kogo ta musanta zargin da ake yi wa gwamna Usman Ododo da cewa shi ya boye shi.

EFCC ta yi barazanar neman taimakon sojoji domin cafke tsohon gwamnan idan ya ci gaba da kin bin doka da oda.

Da yake mayar da martani a kan ikirarin da Bello ya yi cewa EFCC ta ki bin umarnin babbar kotun jihar Kogi ta neman kama shi tare da gurfanar da shi a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, Falana ya ce ikirarin ba shi da tushe ko kadan.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta bi umarnin babbar kotun jihar Kogi ta hanyar gurfanar da Bello bisa zargin almundahanar kudi sama da N80bn.

Ya bayyana umarnin da babbar kotun tarayya ta bayar na kama Bello domin gurfanar da shi a matsayin wanda ya yi daidai da umarnin babbar kotun jihar Kogi.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Gwamnatin Jigawa Na Ƙarfafa Ilimin Addinin Musulunci -Ado Maje Sale

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano