Za A Yi Taron Tantance Jaruman Fim Ɗin Ƙwaryar Sama A Kano

DAGA MUKHTAR YAKUBU

Idan Allah ya kaimu gobe Alhamis 10 ga Yuli za a yi taron tantance Jaruman da za fito a sabon ɗin Ƙwaryar sama wanda za a fara ɗauka nan da ‘yan kwanaki kaɗan masu zuwa.

Fim ɗin wanda fitaccen Furodusa Zahraddin Jalabi ya ɗauki nauyin shiryawa, kuma Furodusa Usman Ahmad Usee zai kasance mai kula da shirin. Sai kuma Yunusa Mu’azu da Nura Mai Shabbabu Mubarak za su kasance masu bayar da umarni. Sai kuma marubuci Aminu Idris Abdullahi.

Taron tantancewar na maza da mata zai kasance a tun daga misalin ƙarfe 10 na safe har zuwa yamma a harabar gidan talbijin na Abubakar Rimi ARTV da ke titin Maiduguri a Unguwar Hotoro da ke cikin garin Kano. Ana sa ran za a samu halartar manyan baƙi kamar Shugaban Hukumar tace finafinai ta Jihar Kano Abba El-Mustapha, Shugaban Ƙungiyar Arewa Film Mekars, ƙungiyar Jarumai da na MOPPAN.

Don haka Furodusa Zahraddin Jalabi yake gayyatar dukkan masu sha’awar shiga cikin fim ɗin ko kallon yadda tantancewar za ta kasance da su halarci wajen taron da misali ƙarfe 10 na safiyar ranar Alhamis ɗin domin shiga cikin tantancewar ko kallon yadda za ta kasance.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?