Za Mu Riƙe Amanar Da Dakta Rabi’u Kwankwaso Ya Ɗora Mana Don Kawo Gyara A Doguwa -Hon Ali Abdu

Daga Ibrahim Muhammad Kano

An bayyana cewa aure tsakanin Ango da Amarya ana yin sa ne a bisa soyayya, yarda da gamsuwa tsakaninsu, za su zauna tare kamar yadda Allah ya haɗa su da kyakkyawan burin cimma manufa ta alheri a rayuwarsu.

Jagoran Kwankwasiyya na ƙaramar hukumar Doguwa, kuma mai bai wa Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf shawara a kan tsare- tsaren siyasa, tsohon shugaban ƙaramar hukumar Doguwa a karo biyu, Hon. Ali Abdu Doguwa ne ya bayyana hakan a ɗaurin auren ɗan Kwamishinan Ilimi na jihar Kano, Gwani Ali Bukar Makoɗa.

Ya ce zaman aure sai an yi haƙuri a tsakani, domin daga aure ne ake gina wata al’umma da Allah ne ya san ‘ya’ya da za su haifa a rayuwa da alherin da zai biyo baya a rayuwar Ango da Amarya.

Hon. Ali Abdu Doguwa, wanda tsohon Kwamishina ne na dindindin a jihar Kano, kuma tsohon mai bai wa tsohon Kakakin Majalisar Tarayya, Olufemi Hakeem Gbajabiamila CFR shawara ya ce, uban Ango da aka ɗaura wa aure Kwamishinan Ilimi na jihar Kano Gwani Ali Bukar Makoɗa yayansu ne, kuma mai gidansu, mutumin arziƙi ne da hakan tasa ɗimbin al’umma suka zo suka shaidi ɗaurin auren ɗansa da taya shi fatan alheri.

Hon. Ali Abdu Doguwa ya ce, a matsayinsa na Jagoran Kwankwasiyya na ƙaramar hukumar Doguwa, wanda jagoransu na Kwankwasiyya Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso ya ɗora shi, ya ba shi amana ne don kawo gyara a tsarin Kwankwasiyya a Doguwa, kuma suna aiki tuƙuru don cimma nasara.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun