Habu Fagge Ya Cira Wa Gwamna Abba Kabir Yusuf Hula

Daga Ibrahim Muhammad

Shugaban Hukumar Amintattu na asusun fansho na jihar Kano, Alhaji Habu Muhammad Fagge ya mika gaisuwar sabuwar shekara ga mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf da al’ummar jihar Kano.

A cikin saƙon nasa, ya bayyana fatan alheri, haɗin kai, da ci gaba yayin da jihar ta fara sabon babi a shekarar 2025.

Ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa da wajen ci gaban jihar Kano.

Shugaban amintattu na hukumar fansho ta jihar Kano ya bayyana ƙoƙarin Gwamnan na bunƙasa ci gaba da magance muhimman buƙatu, inda ya jaddada ƙudirinsa a matsayinsu na shugabanni a Hukumar Fansho na tallafa wa manufofin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na biyan kudaɗen fansho da garatuti a kan kari.

Shugaban kwamitin amintattu na fansho na jihar Kano, Alhaji Habu Muhammad Fagge ya ƙarƙare saƙon nasa da yin kira ga al’umma su bai wa gwamnatin Kano haɗin kai da goyon baya domin samar da makoma mai kyau ga jihar.

Ya yi wa kowa fatan alheri da addu’ar ingantar zaman lafiya da bunƙasar arziƙi da nasarar al’ummar Kano da ƙasa baki ɗaya a sabuwar shekarar nan ta 2025.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe