Abba Kabir Yusuf Ɗan Amana Ne -Hon. Bombay Gama

Daga Ibrahim Muhammad

Jigo a jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya a ƙaramar hukumar Nasarawa, Hon. Muhammad Adamu Bombay Gama, ya bayyana cikar Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf shekaru 62 a duniya a mstsayin alheri bisa dama da ya ba shi ta hidimtawa al’ummar jihar Kano.

Ya ce suna mutuƙar farin ciki da ƙarin shekaru da Abba Kabir Yusuf ya yi, domin mutum ne fasihi jajirtacce mai biyayya ga na gaba da shi, wanda a shekaru 62 ɗin nan saboda amana da biyayyarsa ta sama da shekaru 40 yana tare da jagoransu Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso a aiki da hidima da siyasa, ba a taɓa samun wata matsala a tsakaninsu ba.

Hon. Muhammad Adamu Bomboy ya ƙara da nuni da cewa wannan ya nuna Gwamna Abba Kabir Yusuf mutum ne ɗan amana mai gaskiya da ya san karamci da biyayya.

Bombay ya ce suna daɗa godiya ga Allah da ya ba su injiniya Abba Kabir Yusuf a matsayin zaɓaɓɓen Gwamnan jihar Kano da a cikin kusan shekaru biyu da soma mulkinsa yana hidimtawa mutane ta yi musu ayyuka managarta na ci gaban da bunƙasa cigaban jihar Kano a fannoni da dama.

Hon. Muhammad Adamu ya yi addu’ar fatan alheri da ƙarin shekaru masu yawa da albarka ga Gwamna Abba Kabir Yusuf don ya samu dama ta cigaba da hidimtawa al’ummar Kano.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe