Ba Mu Gamsu Da Yadda Aka Yi Aikin Gyaran Filin Wasa Na Sani Abacha Ba -Kwankwaso

Daga Ibrahim Muhammad

Kwamishinan wasanni da matasa na jihar Kano, Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, ya nuna rashin gamsuwarsa game da gyaran filin wasa na Sani Abacha da ke Ƙofar Mata, Kano.

Kwankwaso a wata tattaunawa da ya yi da ‘yan jarida ya ce, “Babu shakka akwai kurakurai wajen gyara filin wasan, wanda na jawo hankali a kan hakan tun da fari,” in ji shi.

Ya buƙaci Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf da ya kafa wani kwamiti da zai binciki yadda aka yi aikin domin gano gaskiya abin da ya faru.

Ya ƙara da cewa wannan gyara da aka yi mataki na farko ne, akwai sauran ayyuka da suka haɗa da gyara wajen gudu na filin da wajen zama na manyan baƙi da ofishin ma’aikata da ke filin wasan.

Kwankwaso ya zargi wasu marasa kishin jihar Kano da yi wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars zagon ƙasa domin a ɗauke ta daga jihar Kano.

Ya jinjina wa Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf bisa nuna kulawa da yake ga ƙungiyar da kuma ci gaban matasan jihar Kano.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe